A yau Lahadi ne shugaba Bola Ahmed Tinubu zai karɓi takardar shaidar jam’iyyar APC a matsayin ɗan takarar shugabancinta a zaɓen 2027.
Kwamitin zaɓen fidda gwani na shugaban ƙasa zai gabatar da takardar shaidar da tutar a cibiyar taro ta ƙasa da ƙasa ta Bola Ahmed Tinubu da ke Abuja bayan tattara sakamakon zaɓen fidda gwani a faɗin ƙasar.
Gwamnonin APC, membobin kwamitin zartarwa na ƙasa, kwamitin aiki na ƙasa, da majalisar dokoki ta ƙasa, tare da jiga-jigan jam’iyyar, za su halarci taron.






























