Musulmai fiye da miliyan 1.5 ne ke gudanar da aikin Hajji a Saudiyya.
Aikin Hajji ɗaya ne daga cikin ginshiƙan addinin Musulunci, wanda ake son kowane Musulmi ya yi idan ya samu hali.
A Yau Talata, 26 ga watan Mayun 2026 ne ake gudanar da hawan Arfa na aikin Hajjin shekarar 1447 bayan Hijira.
A cewar malamai, ranar Arfa ce mafi falala a cikin ranaku.
Sheikh Isa Ali Pantami ya ce ranar Arfa ita rana mafi daraja cikin ranakun shekara da Allah ya hallita.
”Kamar yadda a cikin darare babu daren da ya kai na laylatul qadar falala, haka ma a cikin ranaku babu wadda ta kai ranar Arfa falala da daraja a wajen Allah”, in ji Sheikh Pantami.
Sheikh Pantami ya ce saboda daraja da falalar ranar Allah S.W.T da kansa ya ambaci sunan ranar a cikin Alqur’ani mai girma, cikin suratul Bakara aya ta 198.
Shehin malamin ya ce a ranar ce kuma Allah ya cika wa bayinsa addininsa.






























